Saraki ya fita daga APC

 

Shugaban Majalisar Dattijan Najeriya Bukola Saraki ya bayyana ficewarsa daga jam’iyya mai mulki a kasar, APC.

Shugaban ya bayyana hakan ne a shafinsa na Twitter ranar Talata.

“Ina sanar da ‘yan Najeriya cewa bayan tattaunawa, na yanke shawarar fita daga jam’iyyar APC,” in ji shi.

Sai dai kawo yanzu Sarakin bai bayyana jam’iyyar da zai koma ba tukunna. Kuma jam’iyyar APC ba ta mayar da martani ba kan batun.

Hakazalika Gwamnan jihar Kwara Abdulfatah Ahmed shi ma ya bayyana fitarsa daga jam’iyyar, sai dai shi ya bayyana cewa ya koma jam’iyyar adawa ta PDP.

Saraki da Gwamna Abdulfatah wadanda tsofaffin ‘yan jam’iyyar PDP ne, sun koma jam’iyyar APC ne a shekarar 2014.

A makon jiya ne Gwamnan jihar Benue Samuel Ortom shi ma ya sanar da ficewarsa daga jam’iyya mai mulki ta APC zuwa jam’iyyar PDP.

A farkon watan ne Kotun Kolin kasar ta wanke Saraki kan zargin karya wajen bayyana kadarorinsa.

Wadanda suka fice daga APC a kwanan nan

Jam’iyyar APC ta kauce hanya – Buba Galadima
  • Gwamnan jihar Benue Samuel Ortom
  • ‘Yan majalisar dokoki ta kasa 52 sun sauya sheka daga APC zuwa PDP
  • Bangaren Akida da Restoration a jihar Kaduna wadanda ke rigima da Gwamna Nasir el-Rufa’i
  • Suna dai samun goyon bayan Sanata Shehu Sani da Sanata Suleiman Hunkuyi
  • Bangaren rAPC na Buba Galadima ya kulla alaka da PDP domin kayar da APC a 2019 – wasu na ganin su ma sun kama hanyar ficewa daga jam’iyyar
  • Sanata Abdul-Azeez Nyako da Dan majalisar Wakilai Rufai Umar daga Adamawa – kamar yadda Daily Trust ta rawaito
  • Hakeem Baba Ahmed – shugaban ma’aikata a ofishin Shugaban Majalisar Dattawa Bukola Saraki
  • Usman Bawa – mataimaki na musamman ga Kakakin Majalisar Wakilai Yakubu Dogara.

More News

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miĆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaĆ™i da yiwa tattalin arzikin Ć™asa ne ya hana shi bayyana...