[ad_1]
Aci gaba da kakar sauyin sheka a farfajiyar siyasar Najeriya,mun samu labari cewar Sanata mai wakiltar EDO ta Arewa Sanata Francis Alimikhena na shirin ficewa daga jam’iyyar APC zuwa Jam’iyyar PDP
A lokacin da yake karin haske dangane da lamarin a birnin Benin,mai magana da yawun sanatan Mr. Adoga J. Ibrahim ya bayyana cewar Sanatan yana fuskantar tsangwama daga shugaban jam’iyyar na kasa kuma tsohon gwamnan jihar ta Edo Adams Oshiomole da ita kanta jam’iyyar da maduhunta Bola Ahmad Tinubu dangane da zargin da suke yi masa na daukan tsagin ra’ayin jam’iyyar PDP a majalisa da kuma goyon bayan Bukola Saraki ,baya ga bijirewa umarnin jam’iyyar APC da ra’ayinta a bahallatsar dake faruwa dangane da ahugabancin majalisar.
“Wannan dalili ne yasa tilas sanatan yabi maigidansa kakakin majlisar ta dattijai wato Bukola Saraki.” Inji Mr.Adoga
[ad_2]