Sabon sufeton ‘yan sanda zai yi wa rundunar garambawul

A makon da ya gabata ne Shugaba Buhari ya nada sabon Sufeto Janar din

A makon da ya gabata ne Shugaba Buhari ya nada sabon Sufeto Janar din

Sabon Sufeto Janar na ‘yan sandan Najeriya, Mohammed Abubakar Adamu ya sanar da wasu garambawul a ayyukan rundunar.

Sauye-sauyen sun hada da mayar da runduna ta musamman mai yaki da fashi da makami, SARS karkashin kwamishinonin yan sanda na jihohi.

Ya kuma rusa duk sassan da ke gudanar da bincike kamar Kwamitin Jami’ai masu bincike na musamman.

Haka kuma, ya sanar da cewa zai yi gyaran fuska a yadda rundunar ke tattara bayanan sirri da yin bincike da kuma ayyuka na musamman na rassan rundunar kan yaki da ta’addanci da sashen da ke bayar da kariya na musamman.

Wannan ne dai taronsa na farko da kwamishinonin ‘yan sanda da sauran manya a rundunar.

Taron na sirri zai duba matakan tsaro da rundunar za ta dauka a lokacin zabe mai zuwa. A makon jiya ne dai Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya nada sabon babban sufeton riko na ‘yan sandan kasar.

Ya maye gurbin Ibrahim Idris, wanda ya sauka daga kan mukaminsa bayan ya kai shekara 60 da haihuwa kamar yadda doka ta tanada.

More News

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...