Rubewar hakori: kun san yanda zaki ke kassara lafiyar hakoran yara?

Rashin kula na daga cikin abubuwan da suka sa yara a Afirka suka fi fama da ciwon hakori

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Likitocin hakori a Birtaniya sun bukaci gwamnatin kasar da ta sa makarantun kasar su daina bai wa yara cimaka mai zaki domin maganace rubewar hakora.

Sun ce hakan na da alfanu domin shawo kan matsalar wadda ke addabar kimanin kashi daya cikin hudu na yara ‘yan shekara biyar.

Haka nan masanan a harkar lafiya na bukatar ganin an kara sanya ido kan yadda yara ke wanke baki.

Kafin sauka daga mukami, Firaminista Theresa May ta sanar da wasu shirye-shirye na bunkasa lafiyar hakoran yara.

Sai dai sashin lafiyar hakori na kasar ya ce duk da an samu ci gaba a fannin, akwai bukatar a kara azama.

Wani kwararren likita a Najeriya Dakta Tanko Zakari, na asibitin koyarwa na Aminu Kano ya ce yara a yankin nahiyar Afirka sun fi na yankin Turai fama da wannan matsala ta rubewar hakori.

Ya ce, yawancin abubuwan da ke haddasa wannan matsala shi ne rashin ilimi da kuma hangen nesa game da lafiyar yara.

Sai dai ya ce matakin rage shan zaki, da kuma rungumar dabi’ar wanke baki za su iya hana rubewar hakora.

A cewarsa ‘ya kamata iyaye su tabbatar yara na wanke baki a kowane lokaci, a lokacin da za su tafi makaranta, da kuma lokacin da za su kwanta bacci.’

Shi dai bangaren kula da lafiyar hakorin na Birtaniya ya fitar da wani rahoto, inda ya bayar da shawarar daukan wasu matakai domin shawo kan matsalar rubewar hakori ga yara.

Shawarwarin sun hada da:

  • Dukkanin makarantu su fito da tsarin lura da yadda yara ke goge hakori.
  • Dukkanin makarantu su daina bai wa yara abinci mai sukari kafin shekarar 2022.
  • A takaita tallace-tallacen abinci masu dauke da sukari sosai.
  • A rage sukari da ake sanyawa cikin abincin jarirai da kamfanoni ke hadawa.

More News

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miĆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaĆ™i da yiwa tattalin arzikin Ć™asa ne ya hana shi bayyana...