Rikici tsakanin ‘yan Najeriya da Kenya a kan Lupita

Lupita

Hakkin mallakar hoto
AFP

Fada ya kaure tsakanin ‘yan Najeriya da takakwarorinsu na kasar Kenya a shafin twitter saboda zabar wata jaruma ‘yar kasar Kenya, Lupita Nyong’o ta fito a matsayin ‘yar Najeriya a wani shirin fim.

Fim din mai suna Americanah, labari ne na wata mata ‘yar Najeriya da ta je karatun jami’a a Amurka da kuma dawowarta Legas.

An samo labarin dake fim din Americanah ne daga wani littafi wallafar Chimamanda Ngozie Adichie, wanda ya yi fice har ya samu babbar kyauta a 2013.

Tun bayan sanarwar da kamfanin shirya fina-finai na WarnerMedia ta fitar a makon jiya, ‘yan Najeriya ke ta nuna adawarsu a shafin twitter, cewa bai dace a zabi Nyong’o ‘yar kasar Kenya, wacce ta taba lashe kyautar jarumar fim na Oscar ba, ta fito a matsayin ‘yar Najeriya a fim din.

A cewarsu, zai fi dacewa a sanya ‘yar Najeriya da za ta iya magana da harshen ‘yan Najeriya ta fito a matsayin ‘yar kasar.

“Fitowar Lupita a matsayin zai fuskanci matsala daya… magana da harshen Ibo,” a cewar wani a twitter.

Wannan kuma na cewa: “Akwai kyawawan jarumai mata ‘yan Najeriya da za su fi iya yin abun da ake bukata.”

A nasu bangaren, ‘yan Kenya a shafin twitter sun yi ta kare zabin da aka yi wa Nyong’o, inda suke wa ‘yan Najeriya shagube da cewa ai ba Nyong’o ce ta “kawo rashin aikin yi a Najeriya ba” saboda ta zama kwararriyar jaruma.

Wasu kuma sun tunatar da ‘yan Najeriyar cewa ba a sanya dan yankin gabashin Afirka ko daya ba a wakar Beyoncé da aka sanya fim din ‘The Lion King’ wanda kamfanin Disney ya sabunta, duk da cewa an yi amfani da yanayin kurmin kasar Kenya wajen tsara fim din.

[ad_2]

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...