Rikici na ta′azzara a Birinin Kudus | Labarai

Rikici ya sake barkewa tsakanin ‘yan sandan Isra’ila da Falasdinawa a harabar Masallacin Al-Aqsa da ke birnin Kudus a daidai lokacin da Falasdinawa ke ibadun neman yin gamon katar da daren lailatul kadri.
Kungiyar bayar da agaji ta Red Cross a yankin Falasdinu, ta ce fiye da mutane 90 ne suka jikkata galibi kananan yara wadanda harbin harsashen roba da gurneti mai sa kwalla ya raunata.
Wannan dai shi ne rikici mafi muni da aka taba gani a ‘yan shekarun baya-bayan nan a yankin, a ci gaba da ke Allah wadarai da matakin Isra’ila na korar Falastinawa don gina wa Yahudawa matsuguni a binrin Kudus da Falasdinawa ke yi.

More News

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...