Rashin aikin yi da talauci shi ya haifar da Boko Haram—OBJ

Tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo ya ce a farkon rikicin Boko Haram a yankin Arewa-maso-Gabas, wadanda suka kafa kungiyar ta’addancin sun shaida masa cewa talauci da rashin aikin yi ne ya jefa su cikin wannan aika-aika.

Sai dai ya yi gargadin cewa sama da yara miliyan 20 da ba sa zuwa makaranta a kasar nan za su iya zama ‘yan Boko Haram nan gaba idan ba a gaggauta magance su ba.

Ya bayyana haka ne a wajen kaddamar da wani littafi mai suna, ‘Pillars of Statecraft: Nation-building in a change world’ wanda ‘yarsa, Dokta Kofo Obasanjo-Blackshire ta rubuta a wani taron da aka yi a Legas.

Da yake amsa tambayar daya daga cikin mahalarta taron kan dalilin da ya sa manufofin gwamnati suka zama siyasa fiye da na mutane a ‘yan kwanakin nan, ya ce wani bangare na manyan matsalolin kasar nan shi ne a kullum ana neman wanda za a daura wa alhakin matsalolinta ne.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]