Rashin aikin yi da talauci shi ya haifar da Boko Haram—OBJ

Tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo ya ce a farkon rikicin Boko Haram a yankin Arewa-maso-Gabas, wadanda suka kafa kungiyar ta’addancin sun shaida masa cewa talauci da rashin aikin yi ne ya jefa su cikin wannan aika-aika.

Sai dai ya yi gargadin cewa sama da yara miliyan 20 da ba sa zuwa makaranta a kasar nan za su iya zama ‘yan Boko Haram nan gaba idan ba a gaggauta magance su ba.

Ya bayyana haka ne a wajen kaddamar da wani littafi mai suna, ‘Pillars of Statecraft: Nation-building in a change world’ wanda ‘yarsa, Dokta Kofo Obasanjo-Blackshire ta rubuta a wani taron da aka yi a Legas.

Da yake amsa tambayar daya daga cikin mahalarta taron kan dalilin da ya sa manufofin gwamnati suka zama siyasa fiye da na mutane a ‘yan kwanakin nan, ya ce wani bangare na manyan matsalolin kasar nan shi ne a kullum ana neman wanda za a daura wa alhakin matsalolinta ne.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]