Rabi’u Kwankwaso: Tsohon gwamna ya ce jama’ar Kano sun fi bukatar ilimi ba gada ba

Sanata Rabiu Musa Kwankwaso

Tsohon Gwamnan jihar Kano da ke Arewa maso Yammacin Najeriya, Senata Rabiu Musa Kwankwaso ya soki lamirin gwamna mai ci, Abdullahi Ganduje game da shirin gwamnatinsa na karbar rancen naira biliyan ashirin don aiwatar da aikin gina gada a birnin Kano.

Senata Kwankwaso ya ce ba dai-dai ba ne gwamnati ta ci bashin da zai bar al`ummar da za a haifa nan gaba da dawainiyar biya.

A tattaunawarsa da BBC, tsohon gwamnan Kanon ya ce hakkin gwamnatin tarayya ne ta gina gadar, wadda ta hada birnin Kano da hanyar zuwa Wudil.

A cewarsa, “maimakon gwamna ya je ya ga Buhari ya ce da shi ka zo ka yi mana gada, bai yi ba, gadojin da muka yi a Kano gaba dayansu da kudin gwamnatin wannan lokaci muka yi”.

Kwankwaso ya kara da cewa duk da ana bukatar gada a Kano, amma abin da mutanen jihar suka fi bukata shi ne ilimi – “a koya wa yayan talakawa aikin sana’oi na hannu wanda yara za su iya rike kansu”. in ji sa.

Ya kuma soki yadda gwamna Ganduje yake sayar da filaye lamarin da a baya-bayan nan ya janyo ce-ce-ku-ce.

Da yake magana kan makomar filayen da gwamnatin Kano ke sayarwa kuwa, tsohon gwamnan jihar Kanon ya bayyana cewa matukar mulki ya koma hannunsu, toh ba makawa sai an rushe gine-ginen da aka aza kan filayen.

“Duk wani gurin hukuma, mutum ko ya yi bene hawa dubu a ruguzo shi, a share gurin a mayar da shi yadda yake da”, a cewar Kwankwaso.

More News

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miĆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaĆ™i da yiwa tattalin arzikin Ć™asa ne ya hana shi bayyana...