A cigaba da ziyarar da yake kaiwa yankunan da ambaliyar ruwa ta yiwa barna a kasarnan, mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo ya ziyarci jihar Anambra a yau ranar Alhamis.
Osinbajo ya kewa wuraren da ambaliyar ruwan ta yi mummunan barna.
Mataimakin shugaban kasar ya samu rakiyar gwamnan jihar Anambra, Willie Obiano da kuma ministan kwadago Chriss Ngige.
A lokacin da yake zagayawa wuraren a cikin kwale-kwale Osibanjo ya jajantawa mutanen da abin ya shafa inda ya ce gwamnatin tarayya za ta tallafa musu.
“A yau ina daya daga cikin wuraren da ambaliyar ruwa ta shafa a Otuocha dake Anambra domin ganin halin da yan uwan mu mata da maza suke ciki abin akwai kada zuciya.Zamu samarwa wadanda abin ya shafa abinci da kuma kayan agaji.muna jajanta muku.”Osinbajo ya ce.
A farkon makon nan ne gwamnatin ta tarayya ta ayyana dokar ta baci kan ambaliyar ruwan bayan da mutane sama dari suka rasa rayukansu da kuma asarar dukiya ta biliyoyin naira.