Nijar ta samu tallafi maganin malaria daga Amurka

Sauro ne ke haddasa cutar malaria

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Gwamnatin Amurka ta tallafa wa jamhuriyar Nijar da magungunan zazzabin cizon sauro wato malaria na milyoyin CFA.

Tallafin dai ya hada da magungunan rigakafin zazzabin cizon sauro dama na magance cutar da zarar an kamu da ita.

Kazalika daga cikin tallafin da Amurkan ta ba wa Nijar, akwai gidajen sauro.

Amurka dai ta bayar da wannan taimako ne ga Nijar da zimmar rage yaduwar cutar ta malaria da akshi 50 cikin 100.

Wannan tallafi na Amurkan, na daga cikin wani tsari ne na kasar wajen tallafa wa kasashe masu tasowa.

Cutar zazzabin cizon sauro na daga cikin cututtukan da ke saurin kisan kananan yara da ma mata masu juna biyu a kasar.

Gwamnatin Nijar ta kasa yakin da take a kan yaduwar cutar zuwa gida uku da suka hada da neman tallafi da wadatar da al’ummar kasar da maganin rigakafin cutar da kuma tsaftace unguwanni.

Kasashen Afrika ne suka fi fama da cutar zazzabin cizon sauro, kuma yawancin wadanda ke mutuwa yara ne.

More News

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...