NFF da kulob din Roma sun kulla yarjejeniya | BBC Hausa

Shugabannin NFF (Amaju Pinnickda) da AS Roma (Jim Pallottane) ne da mataimakansu a wurin taron kulla yar

Hakkin mallakar hoto
NFF

Image caption

Shugabannin NFF (Amaju Pinnickda) da AS Roma (Jim Pallottane) ne da mataimakansu suka halarci taron

Hukumar Kwallon Kafa Ta Najeriya NFF ta kulla yarjejeniyar aiki tare da kungiyar kwallon kafa ta AS Roma mai buga gasar Serie A ta Italiya.

Bisa ka’idojin yarjejeniyar, Roma da Hukumar Kwallon Kafa Ta Najeriya za su rika gudanar da harkokin da suka shafi wasanni a ciki da wajen fili, kamar yadda bangarorin biyu suka bayyana ranar Juma’a.

Bangarorin biyu za su rika taimaka wa juna wajen ci gaban harkokin wasanni da suka hada da shawarwari game da horar da matasan ‘yan wasa daga Najeriya da kuma koyar da kulob-kulob a Najeriya yadda za su rika tafiyar da shafukansu na sada zumunta.

Ita kuma NFF za ta taimaka wa Roma wajen gina nata harkokin a Najeriya.

Kazalika, a watanni masu zuwa jami’an hukumar ta NFF za su yi tattaki zuwa birnin Rome domin ganin yadda kungiyar matasa ta Roma ke gudanar da wasanninsu.

Hakan zai ba su dama wurin gina matasa da kuma kungiyoyinsu a harkar wasanni a gida Najeriya.

Shugaban kungiyar ta Roma Jim Pallotta ya ce tun a 2018 suka fara aiki da Super Eagles yayin gasar cin Kofin Duniya a kasar Rasha.

“Rukunin ma’aikatanmu sun fara aiki tare da Super Eagles a 2018 a shafukan sada zumunta da kuma lokacin gasar Kofin kasashen Afirka, wanda aka fara da maudu’in #ForzaSuperEagles.

“Mu ne kungiya ta farko daga wajen Najeriya da ta bude shafin Twitter cikin harshen Pidgin mai shelkwata a Lagos.”

Kungiyar za ta duba yiwuwar buga wasan bude ido a Najeriya tare da bude makarantar horar da wasanni.

More News

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...