NDLEA ta bankado kwantena makare da Tramadol a Legas – AREWA News

Hukumar NDLEA dake hana sha da kuma fataucin miyagun kwayoyi ta samu nasarar kama wata kwantena mai tsawon kafa 40 dake dauke da kwayar maganin Tramadol a tashar jirgin ruwa dake Lagos.

Bayanin haka na kunshe ne cikin wata sanarwa da John Achema mai magana da yawun hukumar ya fitar.

A cewar sanarwar, shugaban hukumar,Muhammad Abdallah ya ce kama kwantenar na zuwa ne bayan da a yan kwanaki jami’an yan sanda suka kama wata kwantenar dake makare da Tramadol da kuma wasu magunguna da aka haramta su shigowa da kuma yin amfani da su.

Kamfanin dillancin labarai na NAN ya rawaito cewa, jami’an hukumar dake aiki a Apapa sune suka samu nasarar kama kwantenar dauke da kwayar magani da ake zargin Tramadol ne da kuma Codeine.

Abdullahi, ya ce binciken farko da suka yi ya nuna cewa akwai katan 255 na nau’ikan Tramadol iri-iri.

More News

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye aikinsa na wani lokaci

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa na wani lokaci domin tunkarar matsalar lafiya.Mista Ngelale...

Ali Jita ya koma jam’iyar APC daga NNPP

Mataimakin shugaban majalisar dattawa dattawa, Sanata Barau Jibrin ya karɓi fitaccen mawakin Kannywood, Aliyu Isa Jita daga jam'iyar NNPP ya zuwa jam'iyar APC. Ali Jita...

An yi jana’izar mutumin da ya ƙirƙiri tutar Najeriya

Iyalan marigayi, Pa Taiwo Akinkumi mutumin da ya ƙirƙiro tutar Najeriya sun yi bikin binne shi bayan da gwamnatin tarayya ta gaza cika alƙawarin...

‘Za a ƙara wa ƴan bautar ƙasa na NYSC alawus’

Babban daraktan hukumar yi wa kasa hidima ta kasa (NYSC) Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya tabbatar wa ‘yan bautar kasar cewa za a kara...