NDLEA ta bankado kwantena makare da Tramadol a Legas – AREWA News

Hukumar NDLEA dake hana sha da kuma fataucin miyagun kwayoyi ta samu nasarar kama wata kwantena mai tsawon kafa 40 dake dauke da kwayar maganin Tramadol a tashar jirgin ruwa dake Lagos.

Bayanin haka na kunshe ne cikin wata sanarwa da John Achema mai magana da yawun hukumar ya fitar.

A cewar sanarwar, shugaban hukumar,Muhammad Abdallah ya ce kama kwantenar na zuwa ne bayan da a yan kwanaki jami’an yan sanda suka kama wata kwantenar dake makare da Tramadol da kuma wasu magunguna da aka haramta su shigowa da kuma yin amfani da su.

Kamfanin dillancin labarai na NAN ya rawaito cewa, jami’an hukumar dake aiki a Apapa sune suka samu nasarar kama kwantenar dauke da kwayar magani da ake zargin Tramadol ne da kuma Codeine.

Abdullahi, ya ce binciken farko da suka yi ya nuna cewa akwai katan 255 na nau’ikan Tramadol iri-iri.

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...