NDLEA ta bankado kwantena makare da Tramadol a Legas – AREWA News

Hukumar NDLEA dake hana sha da kuma fataucin miyagun kwayoyi ta samu nasarar kama wata kwantena mai tsawon kafa 40 dake dauke da kwayar maganin Tramadol a tashar jirgin ruwa dake Lagos.

Bayanin haka na kunshe ne cikin wata sanarwa da John Achema mai magana da yawun hukumar ya fitar.

A cewar sanarwar, shugaban hukumar,Muhammad Abdallah ya ce kama kwantenar na zuwa ne bayan da a yan kwanaki jami’an yan sanda suka kama wata kwantenar dake makare da Tramadol da kuma wasu magunguna da aka haramta su shigowa da kuma yin amfani da su.

Kamfanin dillancin labarai na NAN ya rawaito cewa, jami’an hukumar dake aiki a Apapa sune suka samu nasarar kama kwantenar dauke da kwayar magani da ake zargin Tramadol ne da kuma Codeine.

Abdullahi, ya ce binciken farko da suka yi ya nuna cewa akwai katan 255 na nau’ikan Tramadol iri-iri.

More from this stream

Recomended

Mutane 7 Sun Rasa Rqyukansu, 53 Sun Jikkata Sakamakon Guguwar Iska a Jigawa

Akalla mutane bakwai sun rasa rayukansu, yayin da 53 suka jikkata bayan wata guguwar iska ta yi barna a kananan hukumomi 13 na jihar Jigawa. Rahotanni sun nuna cewa guguwar ta shafi gidaje 5,403 a cikin garuruwa 120, inda ta lalata makarantu sama da 47, asibitoci uku, ofisoshin ‘yan sanda biyu, gidajen zama da sauran […]