Najeriya Za Ta Kashe N400B Kan Rigakafi

VOA Hausa

Kudaden dai za ayi amfani da su ne domin yiwa kashi 70 cikin 100 na al’ummar Najeriya rigakafin da yawansu ya kai kimanin miliyan 211.

Da yake yiwa shugaban majalisar dattawa bayani game da shirin, ministan lafiya Osagie Ehanire yace a shirye gwamnatin tarayya take domin ceto ‘yan Najeriya, duba da cewa an shiga zagaye na biyu na annobar korona.

shugaban-faransa-emmanuel-macron-ya-kamu-da-annobar-covid

birtaniya-ba-za-ta-ci-gaba-da-zama-fursunan-covid-19-ba—johnson

najeriya-an-sami-mutum-na-farko-da-ya-rasu-sakamakon-coronavirus

Mai sharhi kan lamuran yau da kullum Bashir Baba yace wannan wani salo ne na kamfatar dukiyar talaka a yayin da matsalar tsaro ke addabar kasar.

Da yake tsokaci kan lamarin Aliyu Shamaki yace tunda annobar cutar korona ta shiga ake fitar da makudan kudaden don yaki da cutar amma har yanzu ‘yan Najeriya basu gani a kasa ba.

Hoton tallafin maganin da madagascar ta baiwa Nijar domin yakar coronavirus
Hoton tallafin maganin da madagascar ta baiwa Nijar domin yakar coronavirus

A nasa bangaren masanin kimiyar siyasar tattalin arziki a jami’ar Abuja Dr. Farouq Bibim Farouq yace duk da lamarin yana da kyau amma kudin yayiwa irin kasashe masu tasowa kamar Najeriya nauyi.

Yanzu dai za’a jira aga yadda lamarin zai kasance lokacin da mutane suka fara sabawa da barazanar annobar.

More News

Gwamnan Kano ya sanya hannu kan dokar yin gwajin lafiya kafin aure

Gwamnan jihar Kano, Engr Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu kan wata doka za ta tilastawa masu yin aure yin wasu gwaje-gwajen lafiya gabanin...

An kashe kwamandan soji a Katsina

An kashe kwamandan sojoji na wani sansanin soji da ke Sabon Garin Dan’Ali a karamar hukumar Danmusa a jihar Katsina a wani harin kwantan...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...