NAFDAC Ta Kama Tan 140 Na Magungunan Da Suka Lalace a Aba

Hukumar NAFDAC ta bankado wuraren ajiya guda biyu da ke cike da magungunan da suka lalace a titin Sam Mbakwe, Aba da ke jihar Abuja.

Wasu daga cikin magungunan an sake liƙe musu sabon lakabin kwanan watan lalacewa kafin jami’an tsaro su isa wurin.

Haka nan a karamar hukumar Osisioma, hukumar ta kwace tan 140 na magungunan da suka lalace, baya ga wasu da aka kama a kasuwar Ariaria.

An kuma tattara samfurin magunguna 178 don gwaji.

NAFDAC ta sha alwashin ci gaba da yaki da safarar magungunan da ke barazana ga lafiya.

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...