Mutum sama da 80 sun mutu a rikicin makiyaya da manoma na Filato

A wani mummunan rikicin da ya barke tsakanin makiyaya da manoma a jihar Filato, akalla mutane 85 ne suka mutu yayin da sama da mutane 3,000 suka rasa matsugunansu, kamar yadda rahotanni suka bayyana a ranar Alhamis.

Mutane 30 ne suka mutu lokacin da rikici ya barke a ranar Alhamis a kauyuka daban-daban na jihar Filato.

Rikicin kabilanci da addini ya dade yana shafar yankin.

A cewar wasu majiyoyi da shaidun gani da ido, rikicin ya ci gaba da faruwa, kuma a ranar Alhamis din da ta gabata, al’ummar kauyuka da dama a yankin Mangu da ke Jihar Filato na ci gaba da fama da shi, inda wasu kuma suka tsere daga gidajensu.

Wasu dalilai da ba a tantance su ba ne suka haddasa hare-haren da aka kai a Mangu a wannan makon, amma kashe-kashen da ake yi tsakanin manoma da makiyaya akai-akai ya kai wani mataki.

Kawo yanzu dai an gano gawarwakin mutane 85 a cewar Mista Daput Daniel, shugaban karamar hukumar.

More News

An Jikkata Jami’an Tsaro A Harin Da Ƴan Bindiga Su ka Kai Wa Ayarin Motocin Yahaya Bello

A jikkata wasu jami'an tsaro a wani hari da yan bindiga su ka kai kan jerin ayarin motocin gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ranar...

Bala Muhammad ya zama shugaban gwamnonin jam’iyyar PDP

An zaɓi gwamnan jihar Bauchi, Bala Muhammad a matsayin sabon shugaban kungiyar gwamnonin jam'iyyar PDP. Siminalayi Fabura zaɓaɓɓen gwamnan jihar Rivers shi ne mataimakin shugaban...

Za mu sake bitar mafi karancin albashi a Najeriya—Tinubu

Shugaba Bola Tinubu ya yi alkawarin sake nazarin mafi karancin albashin ma’aikata domin dacewa da yanayin tattalin arzikin kasar nan. A cewarsa, akwai bukatar...

EFCC na zargin tsohuwar ministar mata a mulkin Buhari da karkatar da naira biliyan 2

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin kasa ta'annati ta titsiye tsohuwar ministar harkokin mata Pauline Tallen kan zargin azurta kai ta...