Tinubu Ya Dawo Abuja Daga Ziyarar Aiki Da Ya Kai  Saudiya da Nezaland

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya dawo Abuja bayan ziyarar aiki da ya kai ƙasashen Saudiya da Nezaland.

A ranar 22 ga watan Afrilu ne shugaban ƙasar ya bar birnin tarayya Abuja ya zuwa ƙasar Nezaland inda ya kai ziyarar aiki.

A lokacin mai magana da yawun shugaban kasar, Ajuri Ngelale ya ce Tinubu ya kai ziyarar ne biyo bayan gayyatar da firaministan ƙasar , Mark Rutte ya yi masa.

Bayan kammala ziyarar ta Nezaland shugaban ƙasar ya wuce ƙasar Saudiya inda ya halarci taron tattalin arziki duniya da aka gudanar a ranakun 28 da 29 ga watan Afrilu.

Tun bayan halartar taron ne ba a ƙara jin ɗuriyar shugaban kasar ba inda wata majiya dake kusa da shugaban ta bayyana cewa ya wuce birnin Paris na ƙasar Faransa a wata ziyara ta ƙashin kansa.

Hakan  ya sa wasu Æ´an adawa ciki har da tsohon mataimakin shugaban Æ™asa Atiku Abubakar suka fara kiraye-kirayen da a bayyana inda shugaban Æ™asar ya ke.

More News

Najeriya za ta dena shigo da man fetur a cikin watan Yuni – Dangote

Aliko Dangote mutumin da ya fi kowa arziki a Nahiyar Afirka ya ce Najeriya za ta daina shigo da man fetur a cikin watan...

An ceto mutane 9 daga wani ginin bene da ya ruguzo a jihar Niger

Mutane 9 aka samu nasarar cetowa daga wani ginin bene mai hawa É—aya da ya ruguzo a yankin Sabon Gwari dake garin Minna babban...

An yi faÉ—a tsakanin masu sayar da waya da sojoji a kasuwar Abuja

Rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya, ta tura jami’an leken asiri zuwa kasuwar Banex – wata kasuwar kayan lantarki da na’urorin sadarwa da ke...

Yawan Mutanen Da Suka Mutu A Wutar Da Wani Matashi Ya Cinnawa Wani Masallaci A Kano Sun  Karu Zuwa 16

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon wutar da wani ya cinnawa wani masallaci a ƙauyen Gadan a...