Mutane sama 100 ne ke neman Ganduje ya nada su kwamishinoni

Mutane sama da 100 ne da suka hada da malaman manyan makarantu,yan siyasa da kuma kwararru ke hankoran darewa gurbin kujerar kwamishina a jihar Kano.

Jaridar Daily Trust ta gano cewa yan siyasar dake neman mukamin sun fito ne daga bangarorin siyasa daban-daban da suka hada da tsagin tsohon gwamna,Malam Ibrahim Shekarau, tsagin tsohon mataimakin gwamna, Farfesa Hafiz Abubakar da kuma tsagin tsohon shugaban hukumar lura da tashoshin jiragen ruwa ta Najeriya, Aminu Dabo.

Wata majiya dake kusa da gwamnatin ta fadawa jaridar cewa kaso 40 ne kacal cikin tsofaffin kwamishinonin ake sa ran za su sake dawowa kan mukamansu.

Majiyar da ta nemi a boye sunanta ta bayyana kaso 60 na tsofaffin kwamishinonin ba za su dawo ba bayan da suka gaza yin kokari a lokacin zangon farko na gwamnatin Abdullahi Umar Ganduje.

More News

Tinubu Ya Dawo Abuja Daga Ziyarar Aiki Da Ya Kai  Saudiya da Nezaland

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya dawo Abuja bayan ziyarar aiki da ya kai ƙasashen Saudiya da Nezaland. A ranar 22 ga watan Afrilu ne...

CBN ya dakatar da kudirinsa na sa bankuna su riƙa cajar kwastomominsu

Babban bankin Najeriya ya umarci bankunan da su dakatar da cajin kudaden ajiya har zuwa ranar 30 ga Satumba, 2024.Babban bankin ya bayyana hakan...

Ƴansanda sun kama likitan bogi

Rundunar ‘yan sanda ta Zone 2, Onikan, Legas, ta kama wani likitan jabu mai shekaru 37, kuma ma’aikacin lafiya, tare da zargin amfani da...

Gwamnan Kano ya sanya hannu kan dokar yin gwajin lafiya kafin aure

Gwamnan jihar Kano, Engr Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu kan wata doka za ta tilastawa masu yin aure yin wasu gwaje-gwajen lafiya gabanin...