Mutane biyar sun mutu sanadiyar fashewar bututun mai a jihar Imo

Rundunar yan sandan jihar Imo ta ce mutanen da basu gaza biyar ne ba suka mutu sakamakon fashewar bututun mai a garin Obiti dake karamar hukumar Ohaji/Egbema ta jihar.

Henry Okoye mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar ya ce lamarin ya faru ne ranar Talata inda ya É—ora alhakin fashewar kan É“arayin É—anyen mai.

Okoye ya ce kwamishinan Æ´an sandan jihar, Aboki Danjuma ya kafa wata tawaga domin su gano musabbabin faruwar lamarin tare da kamo masu laifin da suka tsere.

“Fashewar ya faru ne ranar Talata kuma kusan mutane biyar ne suka mutu. Sun Æ™one Æ™urmus a yanzu muna gudanar da bincike tare haÉ—in gwiwar sauran hukumomin tsaro domin gano ko suwaye suke wa tattalin arzikin Æ™asa zagon Æ™asa,”Okoye ya ce.

“Sun je fasa bututun mai ne kamar yadda suka saba lokacin da abun ya faru.”

More News

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar Æ´an sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Ƴansanda sun kama wanda ya kitsa harin da aka kai wa jirgin ƙasa a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Najeriya a ranar Alhamis, ta sanar da kame wanda ake zargin ya shirya harin da aka kai a jirgin ƙasan Abuja-Kaduna...

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani É“angare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...