Mutane 5 Sun Mutu A Ambaliyar Ruwa A Adamawa

Hukumar bada agajin gaggawa ta jihar Adamawa ADSEMA ta ce mutanen da basu gaza 5 ne ba suka mutu sakamakon ambaliyar ruwa da ta shafi al’ummomi da dama na jihar.

Shugaban hukumar ta ADSEMA, Sulaiman Muhammad shi ne ya bayyana haka a yayin ganawa da manema labarai a Yola.

Muhammed ya ce gidaje da dama da kuma ababen more rayuwa ambaliyar ruwa ta yi awon gaba da su a kananan hukumomin Fufore, Yola South da kuma Mubi North.

Ya ce hukumar ta na gudanar gangamin wayar da kai iri daban-daban kan ambaliyar ruwa a kananan hukumomi 21 na jihar inda ya shawarci mazauna yankin da za a iya fuskantar ambaliyar ruwa da su koma inda wurare masu tudu.

More News

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar Æ´an sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Ƴansanda sun kama wanda ya kitsa harin da aka kai wa jirgin ƙasa a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Najeriya a ranar Alhamis, ta sanar da kame wanda ake zargin ya shirya harin da aka kai a jirgin ƙasan Abuja-Kaduna...

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani É“angare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...