MTN yana ƙoƙarin ƙara kuɗin kati da data a Najeriya

Katafaren kamfanin sadarwa na MTN na kokarin kara kudin katin waya da na data a Najeriya.

Kamfanin sadarwa mafi girma a nahiyar Afirka ya ba da rahoton raguwar ribar da ake samu a duk shekara a ranar Litinin, sakamakon hasarar da ya samu bayan harajin da ya kai Naira biliyan 137 da ayyukanta na Najeriya ke yi da kuma karin kudin gudanar da aiki.

Shugaban Kamfanin na MTN, Ralph Mupita, ya ce tuni kamfanin ya fara tattaunawa da hukumomin Najeriya kan hakan.

“Bisa bayanin yadda ake kashe kudaden mu a Najeriya, muna bukatar karin kudin fita don rage farashin tafiyar da hanyoyin sadarwa,” in ji Mupita. 

More News

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...