Messi zai buga wa Argentina kwallo ranar Juma’a

Lionel Messi

Hakkin mallakar hoto
Quality Sport Images

Image caption

Har ila yau Argentina za ta kara da Uruguay a birnin Tel Aviv a ranar Litinin

Lionel Messi na cikin tawagar da za ta wakilci kasar Argentina a wasan sada zumunci da za ta fafata da Brazil a kasar Saudiyya ranar Juma’a.

Wannan ne karon farko da dan wasan zai fito a wasa irin wannan tun bayan korarsa daga filin wasa a gasar Copa America a fafatawar kasarsa da Chile cikin watan Yuli.

An dakatar da dan wasan na Barcelona, mai shekara 32, har tsawon watanni uku bayan da ya ayyana cewa ana magudi a gasar.

Hakazalika dan wasan Aston Villa Douglas Luiz a karon farko na cikin tawagar da za ta wakilci Brazil a wasan.

Wannan shi ne karo na farko da kasashen biyu biyu za su yi wasa tun bayan da Brazil ta doke Argentina da ci 2-0 a wasan kusa da na karshe a gasar Copa America.

Brazil ta kasa cin nasara a wasanni hudu tun lokacin, da ta sha kaye a hannun Peru da ci 1-0 a watan Satumba, yayin da Argentina ta samu nasara a wasanni hudu a lokacin da aka dakatar da Messi, inda ta doke Ecuador 6-1 a watan da ya gabata.

Har ila yau Argentina za ta kara da Uruguay a birnin Tel Aviv a ranar Litinin, amma ana ganin za a iya dakatar da wasan saboda rikicin da ke faruwa a Isra’ila.

Ita kuwa Brazil za ta kara da Koriya ta Kudu a birnin Abu Dhabi ranar Talata, wanda zai kasance wasansu na karshe kafin fara wasannin share fagen shiga Gasar Cin Kofin Duniya na 2022 da za fara a watan Maris.

More News

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...