Matar aure yar shekara 15 ta sakawa mijinta shinkafar bera

Rundunar yansandan jihar Kano ta kama wata mata aure mai suna Hassana Lawal yar shekara 15 dake kauyen Beci a karamar hukumar Kumbotso ta jihar.

Ana dai zargin matar ne da sakawa mijinta,mai suna Sale Abubakar dan shekara 33 guba a abinci.

Mai magana da yawun rundunar yansandan jihar,DSP Abdullahi Haruna Kiyawa shine ya tabbatar da kamen cikin wata sanarwa da ya fitar.

Haruna ya ce ranar 16 ga watan Afirilu da misalin karfe biyu na rana rundunar ta samu rahoton dake cewa matar da ake zargi ta bawa mijinta abinci da shinkafar bera a ciki.

An dauki mutumin ya zuwa asibitin kwararru na Murtala Muhammad domin samun kulawa.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ya ce tuni suka kaddamar da bincike kan lamarin kuma za a gurfanar da wacce ake zargi gaban kotu da zarar an kammala binciken.

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...