[ad_1]
Mataimakin shugaban majalisar dokokin jihar Kaduna, John Audu Kwaturu da kuma mamba a majalisar dake wakiltar mazabar Kudan a majalisar, Junaidu Yakubu sun sauya sheka daga jam’iyar APC ya zuwa PDP.
Kwaturu wanda ya yi magana da manema labarai ta wayar tarho ya ce ya mika takardar ficewarsa daga jam’iyar ga ofishin jam’iyar na mazabar Kwataru dake karamar hukumar Kachia.
“Na bar jam’iyar APC ya zuwa PDP na bayyana dalilaina na ficewa daga APC a cikin wasikar dana aika zuwa mazabata ta Kwataru.
“Zaku so jin cewa hatta shugaban mazaba ta ya fice daga jam’iyar APC,”ya ce.
Anasa ɓangaren Yakubu ya sanar da ficewarsa daga jam’iyar APC wata wasika mai dauke da kwanan watan 7 ga watan Agusta ya zuwa shugaban mazabar Hunkuyi dake karamar Kudan dake jihar.
[ad_2]