Manhajojin Facebook sun gamu da cikas

Facebook

Kamfanin shafin Facebook na fuskantar matsala mafi tsanani a tarihinsa, inda ake cin karo da matsaloli wajen aiki da wasu daga cikin manhajojinsa na intanet a fadin duniya.

Sai dai kamfanin ya ce yana kokarin shawo kan matsalar.

Baya ga ainahin shafin na Facebook shi kansa, manhajar Messenger da Instagram su ma sun gamu da cikas.

Ba a dai gano abin da ke haddasa matsalar ba, wadda ta fara tun kusan karfe hudu na yamma agogon GMT, wato biyar na yammacin jiya a gogon Najeriya da Nijar.

Masu amfani da shafin Facebook sun iya bude shi amma kuma ba sa iya sanya abubuwa a shafin.

Manhajar Messenger ta waya tana aiki ga wasu amma kuma wasu ba ta yi musu aiki, amma kuma manhajar ta Kwamfutar tebur ba ma a samunta.

Matsalar dai ba ta shafi WhatsApp ba.

More News

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...