Man City ta rage tazara tsakaninta da Liverpool

Man City

Manchester City ta yi nasarar doke West Ham United da ci 2-0 a kwantan wasan mako na 26 da suka kara a Etihad.

Tun farko karawar ta zama kwantai bayan da rashin kyawun yanayi ya sa aka dage fafatawar ta su.

City ta fara cin kwallo ne ta hannun Rodri saura minti 15 a je hutun, bayan hutun ne City ta kara na biyu ta hannun Kevin de Bruyne.

Karo na uku kenan Rodri na ci wa City kwallo kuma na farko a filin wasa na Etihad.

Kuma kungiyar kwallon kafa ta Aston Villa aka ci kwallo tara da ka a tarihin Premier bana, sai West Ham mai guda takwas.

Da wannan sakamakon City ta rage tazarar maki da ke tsakaninta da Liverpool ta daya a teburi daga 25 yanzu ya koma 22.

West Ham tana nan a mataki na 18 da maki 24, bayan buga wasan Premier 26.

City za ta ziyarci Leicester City a wasan mako na 27 a gasar ta Premier ranar 22 ga watan Fabrairu.

Ita kuwa West Ham United za ta ziyarci Liverpool ne ranar Litinin 24 ga watan Fabrairu.

More News

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miĆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaĆ™i da yiwa tattalin arzikin Ć™asa ne ya hana shi bayyana...