Majalisar dokokin jihar Taraba ta amince gwamna Kefas ya ciwo bashin biliyan 206

Majalisar dokokin jihar Taraba ta amincewa gwamnan jihar, Agbu Kefas ya ciwo bashin biliyan 206 da miliyan 778.

An amince masa ya ciwo bashin ne domin aiwatar da wani kwarya-kwaryar kasafin kudi.

Majalisar ta amince da bukatar ne a yayin zamanta na ranar Juma’a.

Bashin za a ciwo shi ne daga bankunan kasuwanci na Zenith, United Bank for Africa, Fidelity da kuma Keystone domin aiwatar da ayyuka daban-daban a jihar.

Joe Bonzena kakakin majalisar dokokin jihar ya ce an zartar da kasafin kudin tare da amincewa a ciwo bashin domin gwamnan ya samu damar bijiro da ayyukan da za su saka walwala a zukatan al’ummar jihar da suka dade suna jira.

More News

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar Æ´an sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Ƴansanda sun kama wanda ya kitsa harin da aka kai wa jirgin ƙasa a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Najeriya a ranar Alhamis, ta sanar da kame wanda ake zargin ya shirya harin da aka kai a jirgin ƙasan Abuja-Kaduna...

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani É“angare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...