Majalisar Dattawa Ta Dakatar Da Sanata Abdul Ningi

Majalisar Dattawa ta dakatar da sanata Abdul Ningi kan zargin da ya yiwa cewa an yi cushen naira tiriliyan 3.7 a cikin kasafin kuÉ—in shekarar 2024 da majalisar ta zartar.

Ningi ya bayyana haka ne a cikin wata hira da yayi da kafar yaɗa labarai ta BBC Hausa inda ya ce Kungiyar Sanatocin Arewa za ta tattauna da shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio da kuma shugaban ƙasa Bola Ahmad Tinubu kan batun.

A yayin zaman majalisar na ranar Talata, Sanata Adeola Solomon daga jihar Ogun shi ne ya gabatar da kuÉ—iri inda sanatoci suka tattauna kan zargin kuÉ—irin ya samu goyon bayan Sanata Ned daga jihar Edo.

Bayan doguwar muhara Sanata Jimoh Ibrahim daga jihar Edo ya bada shawarar da a dakatar Ningi na tsawon watanni.

Amma da yake tofa albarkacin bakinsa kan batun Sanata Asuquo Ekpeyong daga jihar Cross Rivers ya roƙi a rage tsawon dakatarwa zuwa watanni shida.

Amma kuma Sanata Sani Musa daga jihar Niger ya nemi a dakatar da Ningi har tsawon watanni uku sannan a saka shi ya rubuta wasikar bada hakuri.

A ƙarshe shugaban majalisar Sanata Akpabio ya amince a dakatar da Ningi na tsawon watanni uku.

More News

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar Æ´an sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Ƴansanda sun kama wanda ya kitsa harin da aka kai wa jirgin ƙasa a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Najeriya a ranar Alhamis, ta sanar da kame wanda ake zargin ya shirya harin da aka kai a jirgin ƙasan Abuja-Kaduna...

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani É“angare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...