Hukumar Alhazan jihar Nejan ta nuna jin dadi tare kuma da yaba wannan matakin ta kuma bashi takardar yabo ta Musamman kamar yadda Daraktan Ayyuka na hukumar Malam Attahiru Bala Dukku ya tabbatar,
A halin da ake ciki kuma, hukumar Alhazan Nigeria ta kai kara a kotu domin bin kadin mutuwar wani alhajin jihar da ya fado daga saman Na’urar kai mutane saman bene ya mutu a aikin hajjin da ya gabata bisa ga bayanin mukaddashin sakataren hukumar jin Dadin Alhazan jihar Neja Umar Makun Lapai.
Yanzu dai hukumar Alhazan tace ta bude kofar biyan kudin kujerar aikin Hajji mai zuwa da za a kai Naira Miliyan daya a Banki, ta kuma gargadi maniyyata kada su ba wani jami’in hukumar kudi a hannu.
Saurari cikakken rahoton Mustapha Nasiru Batsari.