Ma’akacin Hukumar Alhazai Ya Mayar Wa Gwamnati Rarar Kudin Da Ya Saura

Wani jami’in hukumar alhazai mai suna Muhammad Salish Abubakar mai kula da karamar hukumar Rijau, ya ce bayan ya rabawa Alhazan 75 da ke karkashinsa kudin guzirin dalar Amurka 800, sai ya ga yana da rarar dala dubu 20 (kimanin Naira Miliyan 8 na kudin Najeriya), Shi ne ya dawo da kudin a ofishin Hukumar Alhazan jihar ta Neja saboda, a cewarsa, ba hakkinsa bane.

Hukumar Alhazan jihar Nejan ta nuna jin dadi tare kuma da yaba wannan matakin ta kuma bashi takardar yabo ta Musamman kamar yadda Daraktan Ayyuka na hukumar Malam Attahiru Bala Dukku ya tabbatar,

A halin da ake ciki kuma, hukumar Alhazan Nigeria ta kai kara a kotu domin bin kadin mutuwar wani alhajin jihar da ya fado daga saman Na’urar kai mutane saman bene ya mutu a aikin hajjin da ya gabata bisa ga bayanin mukaddashin sakataren hukumar jin Dadin Alhazan jihar Neja Umar Makun Lapai.

Yanzu dai hukumar Alhazan tace ta bude kofar biyan kudin kujerar aikin Hajji mai zuwa da za a kai Naira Miliyan daya a Banki, ta kuma gargadi maniyyata kada su ba wani jami’in hukumar kudi a hannu.

Saurari cikakken rahoton Mustapha Nasiru Batsari.

More News

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miĆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaĆ™i da yiwa tattalin arzikin Ć™asa ne ya hana shi bayyana...