Likitoci a asibitin kwararru na Yariman Bakura, AYBSH, Gusau a Zamfara sun dakatar da shirinsu na shiga yajin aikin sai baba-ta-gani a ranar 4 ga watan Satumba.
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da kungiyar likitocin Najeriya reshen jihar NMA ta fitar a ranar Juma’a mai dauke da sa hannun shugaban kungiyar na jiha, Dakta Sanusi Bello da sakataren kungiyar, Dakta Murtala Shinkafi.
Ku tuna cewa likitocin sun sanya ranar 4 ga watan Satumba su fara yajin aikin sai baba-ta-gani kan rashin biyansu albashi da alawus alawus da gwamnatin jihar ta yi.
Likitocin sun bayyana cewa gwamnatin jihar ta warware rikicin ma’aikatan cikin ruwan sanyi wanda hukumar NMA ta jihar ta gamsu.