Lamarin tsaro ya tilasta wa gwamnatin Zamfara rufe wasu kasuwannin shanu

Gwamnatin jihar Zamfara ta sanar da rufe kasuwannin shanu a kananan hukumomi biyar na jihar nan take.

Kwamishinan yada labarai da al’adu na jihar Zamfara, Alhaji Mannir Haidara ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a Gusau ranar Lahadi.

A cewar Haidar, kasuwannin shanun da abin ya shafa sun hada da Danjibga da Kunchin-Kalgo a karamar hukumar Tsafe, da kasuwannin shanu na Bagega da Wuya a karamar hukumar Anka, da Dangulbi da Dansadau a karamar hukumar Maru, Dauran a karamar hukumar Zurmi, da Nasarawar Burkullu a karamar hukumar Bukkuyim.

Ya ce rufe kasuwannin shanun na wucin gadi ya biyo bayan taron kwamitin sulhu ne.

“Wannan wani bangare ne na matakan magance matsalolin tsaro a jihar. Gwamnati ta lura da yadda ake saidawa da lodin shanu da ake zargin ‘yan bindiga ne suka sace a kasuwannin da abin ya shafa,” in ji Kwamishinan.

Don haka gwamnati ta yi kira ga hukumomin tsaro da hukumar kula da lafiyar dabbobi da kiwo ta jihar da su tabbatar da bin matakan da suka dace.

More News

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...