Gwamnatin jihar Zamfara ta sanar da rufe kasuwannin shanu a kananan hukumomi biyar na jihar nan take.
Kwamishinan yada labarai da al’adu na jihar Zamfara, Alhaji Mannir Haidara ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a Gusau ranar Lahadi.
A cewar Haidar, kasuwannin shanun da abin ya shafa sun hada da Danjibga da Kunchin-Kalgo a karamar hukumar Tsafe, da kasuwannin shanu na Bagega da Wuya a karamar hukumar Anka, da Dangulbi da Dansadau a karamar hukumar Maru, Dauran a karamar hukumar Zurmi, da Nasarawar Burkullu a karamar hukumar Bukkuyim.
Ya ce rufe kasuwannin shanun na wucin gadi ya biyo bayan taron kwamitin sulhu ne.
“Wannan wani bangare ne na matakan magance matsalolin tsaro a jihar. Gwamnati ta lura da yadda ake saidawa da lodin shanu da ake zargin ‘yan bindiga ne suka sace a kasuwannin da abin ya shafa,” in ji Kwamishinan.
Don haka gwamnati ta yi kira ga hukumomin tsaro da hukumar kula da lafiyar dabbobi da kiwo ta jihar da su tabbatar da bin matakan da suka dace.