Shugaban rukunin kamfanonin NNPCL, Mele kyari ya bayyana dalilin da yasa ake sake samun layuka a gidajen mai.
Dogayen layuka sun fara bayyana a gidajen mai a makon da ya wuce hakan ya sa wasu mutane suka fara zargin cewa za a kara kuÉ—in mai.
Amma da yake magana da yan jarida a fadar shugaban kasa Kyari ya alaƙanta ƙarancin mai da cinkoso da ake samu a wasu hanyoyi abin da yasa wasu direbobi suke bi hanyoyi masu nisa domin kaucewa hakan.
Ya kara da cewa ana samar da man fetur kamar yadda ya kamata sosai kuma gwamnatin tarayya tana aiki tuƙuru domin samar da kuɗaden waje a kasuwar musayar kudade domin dai-daita darajar Naira.