Kungiyar NOVAD Ta Tallafawa Almajirai a Kaduna

An saba ganin kananan yara ‘yan ‘kasa da shekaru 10 na ta gararamba kan tituna da tashoshin mota domin yin bara da kuma neman abin da zasu saka a bakinsu.

Hakan yasa kungiyar ta tara almajirai ta raba musu abinci da sutura da kuma Man shafawa.

A cewar shugaban NOVAD sheik Halliru Maraya, kulawa da almajirai zai taimaka da wajen rage al’amuran tashin hankali, domin kuwa rashin kulawa da su shine dalilin dake sa suna shiga yin abubuwan rashin zaman lafiya.

Shi kuma Rev John Joseph, cewa yayi abin da yara almajirai suke so shine a nuna musu ‘kauna da zumunci, a kuma mutunta su, domin kuwa Allah kadai ya barwa kansa sanin abin da yara zasu zama nan gaba.

Manyan malaman addinan Musulunci da Krista ne suka gudanar da jawaban janyo hankali ga almajiran da suka halarci taron.

Wasu daga cikin almajiran da suka samu cin moriyar wannan taro sun nuna jin dadinsu, tare da cewa tabbas hakan yasa sun ji a jikinsu ana kulawa da su.

More News

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaƙi da yiwa tattalin arzikin ƙasa ne ya hana shi bayyana...