Kungiyar Gwamnonin Arewa Ta Bayyana Goyon Bayan Buhari

VOA Hausa

Gwamnonin Arewan da su ka kira wani taron gaggawa a jihar Kaduna sun ce ba su ji dadin abun da ke faruwa a wasu sassan Najeriya ba. Shugaban kungiyar gwamnonin Arewan kuma gwamnan Filato, Simon Bako Lalong shi ya yi magana a matsayin gwamnonin baki daya.

Yace abinda su ke bukata shi ne masu zanga zangar su jira su ga abinda gwamnati za ta yi a matakin jihohi da kuma gwamnatin tarayya. Ya ce gwamnati ba za ta lamunci yadda wadansu suke fakewa da zanga zangar lumana da matasa su ke yi na neman mafita su tada hankalin al’umma ba.

endsars-shugaba-buhari-ya-yi-jawabin-kwantar-da-hankali

endsars-matasan-arewa-sun-bukaci-gwamnati-ta-kawo-karshen-zanga-zanga

an-fafata-tsakanin-masu-zanga-zangar-endsars-da-yan-kasuwa-a-jos

Gwamnonin Arewan sun yaba da kauracewa zanga-zangar da wadansu matasan Arewa su ka yi sannan kuma su ka ce su na tare da shugaban kasa Muhammadu Buhari. Suka kuma bayyana cewa suna tuntubar gwamnonin kudancin kasar tare da jinjinawa gwaman jihar Lagos inda lamarin ya fi muni.

Jawabin shugaban kasa Muhammadu Buhari jiya Alhamis, da taron gwamnonin Arewa da kuma na gwamnonin kudu maso yamma dai sun sa wasu sa ran ganin wannnan zanga-zanga ta lafa a fadin kasar baki daya.

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari yana jawabi kan zanga zanga

Sai dai masu kula da lamura sun bayyana damuwa ganin shugaban kasar ya maida hankali kan matakan da ya ce gwamnatinsa ta dauka na yaki da talauci a kasar, a maimakon zanga zangar da ta rikide ta zama tashin hankali a wadansu sassan kasar, da kuma rasa rayukan masu zanga zanga da dama a jihar Ikko sakamakon amfani da karfin soji da jami’an tsaro suka yi kan masu zanga zanga a Lekki, lamarin da ya sa gwamnan jihar Babajide Sanwo-Olu ya kafa dokar hana fita ta tsawon sa’oi 24 kafin bada umarnin takaita zirga zirga na tsawon kwanaki uku da nufin shawo kan tashin hankalin.

More News

Tayoyin jirgin saman Max Air sun fashe a Yola

Jirgin saman kamfanin Max Air ƙirar Boeing 737 mai rijistar namba 5N-ADB dake ɗauke da fasinjoji 118 da ma'aikata 6 ya gamu da matsala...

ÆŠan majalisar wakilai ta tarayya ya mutu

Hon. Olaide Akinremi Jagaba mamba a majalisar wakilai ta Najeriya dake wakiltar mazaɓar Ibadan North a majalisar ya mutu. Kawo yanzu babu cikakken bayani kan...

Gwamnan Kano ya sanya hannu kan dokar yin gwajin lafiya kafin aure

Gwamnan jihar Kano, Engr Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu kan wata doka za ta tilastawa masu yin aure yin wasu gwaje-gwajen lafiya gabanin...

An kashe kwamandan soji a Katsina

An kashe kwamandan sojoji na wani sansanin soji da ke Sabon Garin Dan’Ali a karamar hukumar Danmusa a jihar Katsina a wani harin kwantan...