Kotun ɗaukaka ƙara ta tabbatar da zaɓen gwamnan jihar Sokoto

Kotun ɗaukaka ƙara dake Abuja ta tabbatar da zaɓen, Ahmed Aliyu a matsayin gwamnan jihar Sokoto.

Rukunin alkalan kotun su uku sun yi watsi da ɗaukaka ƙarar da jam’iyar PDP da ɗan takararta, Saidu Umar suka yi inda suke ƙalubalantar nasarar da Aliyu ya samu.

Dukkanin alkalan uku sun ce ba su ga dalilan da zai sa su yi gyara ga hukuncin kotun sauraren ƙararrakin zaɓen gwamnan da ya bawa Aliyu nasara ba.

Aliyu da ya yiwa jam’iyar APC takara ya lashe zaɓe da kuri’a 453,661 a yayin da Umar ya samu kuri’a 404, 632.

Amma Umar ya yi zargin cewa gwamnan da mataimakinsa Idris Gobir sun miƙawa hukumar INEC takardun kammala makaranta na jabu domin su samu damar tsayawa takara.

Masu ƙarar sun kuma yi zargin cewa anyi magudi a zaben.

Kotun a hukuncinta na ta tace sun gaza tabbatar da gaskiyar zarge-zarge 6 da suka shigar da kara akansu.

More News

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Ƴansanda sun kama wanda ya kitsa harin da aka kai wa jirgin ƙasa a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Najeriya a ranar Alhamis, ta sanar da kame wanda ake zargin ya shirya harin da aka kai a jirgin ƙasan Abuja-Kaduna...

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani ɓangare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...