Kotu ta hana INEC gudanar da zaben da zai maye gurbin yan majalisar dokokin jihar Rivers da suka sauya sheka

Kotun daukaka dake Abuja ta dakatar da hukumar zabe mai zaman manta ta INEC gudanar da sabon zabe na kujerun yan majalisar dokokin jihar Rivers da suka sauya sheka.

Alkalin kotun, Donatus Okorowo shi ne ya bayar da umarnin a ranar Juma’a.

A ranar 11 ga watan Disamba mambobin majalisar dokokin jihar Rivers 27 suka sauya sheka daga jam’iyar PDP ya zuwa jam’iyar adawa ta APC.

Hakan ya sa kakakin majalisar dokokin jihar, Edison Ehie ya ayyana cewa kujerun yan majalisar babu kowa akansu kuma Ya yi kira ga hukumar zabe ta INEC da ta gudanar da sabon zabe a mazabunsu.

Biyo bayan umarnin shugaban majalisar ne yasa masu sauya shekar garyawa gaban kotu.

More News

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani É“angare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...

Matatar Mai Ta Kaduna Za Ta Fara Aiki A Ƙarshen 2024

Kamfanin Kaduna Refining and Petrochemical Company KPRC ya ce matatar mansa za ta fara aiki a shekarar 2024. Mustapha Sugungun managan matatar man ta KRPC...

Manyan dillalan mai za su fitar da litar man fetur miliyan 300 a wannan makon

Ƙungiyar MEMAN ta manyan dillalan man fetur da dangoginsa ta ce mambobinta sun fara lodin mai har lita miliyan 300 a cikin makon nan...

Kotu ta É—aure mutumin sa ya yi sama-da-faÉ—i da kuÉ—in marayu

Babbar kotu a jihar Borno ta yanke wa Isiyaku Ibrahim hukuncin shekara ɗaya a gidan yari da zaɓin biyan tarar naira dubu 100 saboda...