[ad_1]
Wannan shine Hafizu Magaji na Unguwar Tudun Murtala, Kasurgumin dan fashi da makami kuma Hamshakin Dan-Daba da ya addabi mutanen Yankin Tudun Murtala, Rimin Kebe, Kwana Hudu da wasu sassa na birnin Kano kamar su bakin Kasuwa, bakin Zuwo da Jakara. Yana Sata, Kwace har da Kisan kai a lokaci daba-daban.
Ya fada tarkon jami’anmu lokacin da yayi arangama da yan Vigilante da misalin karfe biyun dare yana kokarin fasa wani Shago kuma kafin kama shi sai da ya Sassari Yan Vigilante akalla guda uku kafin a kai ga nasarar chafke shi.
Daga Kakakin Rundunar Yansandan Jihar Kano SP Musa Majia.
[ad_2]