Kalli hotunan barnar da rikicin ‘yan Shi’a da ‘yan sanda ya haifar | BBC Hausa

Hakkin mallakar hoto
KOLA SULAIMON

Wani dan sanda na tafiya a gefen wata mota da masu goyon bayan shugaban Kungiyar ‘Yan Uwa Musulmi, Sheikh Ibrahim Zakzaky suka kona a kusa da harabar majalisar dokokin Najeriya a Abuja, babban birnin kasar ranar 9 ga watan Yulin 2019.

Hakkin mallakar hoto
KOLA SULAIMON

Masu goyon bayan shugaban ‘yan Shi’an da ke tsare sun yi arangama da jami’an tsaro kuma mutane da yawa sun samu raunuka ciki har da ‘yan sanda biyu kamar yadda hukumomi da shaidu suka bayyana.

Hakkin mallakar hoto
KOLA SULAIMON

‘Yan kwana-kwana na kokarin kashe wutar da ke fitowa daga wata mota bayan arangamar tsakanin jami’an tsaro da magoya bayan Sheikh Ibrahim Zakzaky.

Hakkin mallakar hoto
KOLA SULAIMON

Mummunar arangamar ta jikkata mutane. Wani takalmi a wurin da jini ya zuba yayin rikicin tsakanin jami’an tsaro da mabiya Ibrahim Zakzaky.

Hakkin mallakar hoto
KOLA SULAIMON

An lalata motoci da gine-gine a lokacin taho-mu-gaman. Nan wani wurin tsayuwar ‘yan sanda ne da masu zanga-zangar suka lalata ranar 9 ga watan Yulin 2019.

Hakkin mallakar hoto
KOLA SULAIMON

Kungiyar ‘Yan Uwa Musulmin dai sun musanta zarge-zargen rundunar ‘yan sanda na cewa magoya bayan Ibrahim Zakzaky sun harbi ‘yan sandan uku. Wannan wata motar ‘yan sanda ce da masu zanga-zangar suka lalata.

Hakkin mallakar hoto
KOLA SULAIMON

Wani wurin duba motoci da masu zanga-zangar suka lalata sannan suka yi rubutun nuna kin jinin tsare shugaban kungiyarsu Ibrahim Zakzaky.

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...