Juyin mulki: Jakadun da Tinubu ya tura don yin sulhu sun isa Nijar

Tsohon shugaban mulkin soja a Najeriya Janar Abdulsalami Abubakar da Sarkin Musulmi Sa’ad Abubakar na III sun isa ƙasar Nijar don yin sulhu.

Idan ba a manta ba a ƴan kwanakin baya ne dai sojoji suka kifar da gwamnatin shugaba Bazoum, inda ECOWAS ta nuna fushinta tare da ƙaƙaba wa Nijar ɗin takunkumi, ciki har da datse wutar lantarkin da ake ba su daga Najeriya.

A saboda haka ne Shugaba Tinubu ya naɗa Abdulsalami da Sarkin Musulmi don su je su yi sulhu tare da tattaunawa don shawo kan matsalar.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]