Jirgin sama ya yi hatsari a Legas

Wata ƙaramin jirgi ya yi hatsari a unguwar Oba Akran da ke Ikeja a jihar Legas, kamar yadda gidan talabijin na Channels ta ruwaito.

Kakakin Hukumar Binciken Haɗɗuran Jiragen Sama ta Najeriya (NSIB), Tunji Oketunbi, ya tabbatar da faruwar lamarin a yammacin ranar Talata.

Haka kuma, wani jami’in Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Legas (LASEMA) ya shaida cewa lamarin ya faru ne da yammacin ranar Talata.

More from this stream

Recomended