Jirgin kasa ya kashe wata mata a Abuja

Jirgin kasan da ya taso daga Kaduna zuwa Abuja ya buge wata mata dake cikin mota inda hakan yayi sanadiyar ajalinta.

Hatsarin ya faru ne a yankin Kubwa dake birnin tarayya Abuja.

Wani mutum da ya sheda faruwar lamarin ya fadawa gidan talabijin na Channels cewa lamarin ya faru ne bayan da jirgin ya ci karo da motar matar a dai-dai lokacin da take kokarin tsallaka digar jirgin.

Tuni dai jami’an tsaro suka dauke gawar matar tare da motar da ta makale.

More News

Sojojin Nijeriya sun hallaka ‘yan ta’adda 191 tare da kama 184

Rundunar sojojin Najeriya ta bayyana hakan ne a wata sanarwa wacce aka fitar bayan wani taron manema labarai da rundunar ta yi a Abuja...

Farashin gangar ɗanyen man fetur ya ƙaru zuwa $97

Farashin É—anyen man fetur ya karu sosai a ranar Alhamis inda aka rika sayar da kowacce ganga kan dalar Amurka $97. Farashin man nau'in Brent...

Kungiyar ƙwadago ta NLC ta dage kan tsunduma yajin aiki

Kungiyar ƙwadago ta NLC ta ce babu wata yarjejeniya da ta shiga da gwamnatin tarayya domin ta dakatar da shiga yajin aikin sai baba...

Gwamnatin tarayya ta bayar da hutun ranar samun yancin kan Najeriya

Gwamnatin tarayya ta ayyana ranar Litinin 2 ga watan Oktoba a matsayin ranar hutu domin tunawa da ranar da Najeriya ta samu yan cin...