Jihar Borno ta tsawaita shekarun yin ritaya na ma’aikatan lafiya

Gwamnatin jihar Borno ta ce an tsawaita shekarun yin ritaya na ma’aikatan lafiya a jihar daga shekarun aiki 35 zuwa 40 ko kuma shekaru 65 na haihuwa.

A wata sanarwa da aka aikewa shugabannin kananan hukumomin jihar, daraktan kula da lafiya a matakin farko, Ibrahim Sheriff ya ce tsawaita wa’adin ya fara ne daga watan Janairun shekarar 2022.

Sherif ya kuma ce gwamnatin ta amince cewa ma’aikatan lafiya da suka yi ritaya kafin ko kuma bayan watan Janairun shekarar 2022 za su iya dawowa bakin aiki.

Tun da farko gwamnan jihar Babagana Umara Zulum ya amince da karin shekarun ritaya na malaman makaranta zuwa shekaru 65 ko kuma shekarun aiki 40.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) Æ™arÆ™ashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da Æ™arar da É—an majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]