Jihar Borno ta tsawaita shekarun yin ritaya na ma’aikatan lafiya

Gwamnatin jihar Borno ta ce an tsawaita shekarun yin ritaya na ma’aikatan lafiya a jihar daga shekarun aiki 35 zuwa 40 ko kuma shekaru 65 na haihuwa.

A wata sanarwa da aka aikewa shugabannin kananan hukumomin jihar, daraktan kula da lafiya a matakin farko, Ibrahim Sheriff ya ce tsawaita wa’adin ya fara ne daga watan Janairun shekarar 2022.

Sherif ya kuma ce gwamnatin ta amince cewa ma’aikatan lafiya da suka yi ritaya kafin ko kuma bayan watan Janairun shekarar 2022 za su iya dawowa bakin aiki.

Tun da farko gwamnan jihar Babagana Umara Zulum ya amince da karin shekarun ritaya na malaman makaranta zuwa shekaru 65 ko kuma shekarun aiki 40.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan YaÆ™i Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin Æ™wazon jagorancinsa wajen yaÆ™i da ta’addanci da magance matsalar tsaro a Æ™asar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiÆ™a da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]