[ad_1]
Biyo bayan dambarwar haramtawa Kwankwaso gudanar da taron kaddamar da aniyyarsa ta takarar kujerar shugaban kasa a farfajiyar taro na Eagles Square, jam’iyyar APC ta musanta zargi tare da bayyana cewa ko kadan babu hannunta cikin wannan lamari.
Ko shakka babu an haramtawa tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, amfani da dandalin Eagle Square wajen gudanar da taron bayyana kudirin sa na takarar kujerar shugaban kasa a ranar Larabar da ta gabata.
Kamar yadda wani jigo na kwamitin yakin neman zabe na Kwankwaso, Kwamared Aminu Abdussalam, ya shaidawa manema labarai na BBC cewa an hana su gudanar da wannan taro bayan tuni sun riga da biyan kudi na hayar farfajiyar.
A sanadiyar haka dole kanwar naki ta sanya Sanata Kwankwaso ya gudanar da taron kaddamar da kudirin sa a wani babban Otel na Achida a ranar Larabar da ta gabata.
A yayin musanta zargi dangane da hannun jam’iyyar APC cikin wannan dambarwa ta haramtawa Kwankwaso amfani da farfajiyar Eagles Square wajen gudanar da taron sa, ta bayyana cewa ko kadan ba ta dahannu cikin wannan lamari.
Jam’iyyar a yayin cigaba da wanke kanta ta kuma bayyana cewa, wannan takkadama tsakanin Kwankwaso ne da kuma kamfanin mai zaman kansa dake kula da filin na Eagles Square da ya hana gudanar da taron.
Kamar yadda shafin jaridar Sahara Reporters ya rawaito, jam’iyyar ta wanke hannunta kan wannan zargi cikin wani sako data bayyana a shafinta na sada zumunta.
[ad_2]