Jami’an Tsaro Sun Kwace Gidan Buba Galadima

Ana zargin Buba Galadima da ake rashin biyan bashi da kudin ruwa daga shekarar 2004, wanda ya kai Naira miliyan 349.

Buba Galadima, wanda kafin lamarin ya ta’azzara, ya ce ya ga ‘yan sanda sun mamaye gidan sa amma bai san me su ke nufin aikatawa ba.

Daga bisani an fahimci cewa lamunin banki ne da Buba Galadima ya karba da nufin sayo takin zamani, amma a cewar sa, don hukumar binciken manyan laifuka ta Amurka FBI na binciken bankin shi yasa aka ki karbar takardar shaidar lamunin.

Ya zuwa locacin da wakilin Muryar Amurka Nasiru Adamu el-Hikaya ya ke hada wannan labarin, jami’an tsaro sun umurci duk jama’ar da ke cikin gidan da su fice don za a karbi gidan a matsayin ajiya don biyan bashin kudin.

Buba Galadima ya ce sam ba zai fita daga gidan ba.

Za’ a jira a ga yadda wannan lamari zai kaya don tuni wasu su ka fara alakanta shi da siyasa duk da cewa Injiniya Galadima bai ambata hakan ba.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]