Isra’ila za ta kara mamaye wani yankin Falasdinawa

Israel could begin the annexation process next week

Hakkin mallakar hoto
AFP

Image caption

Isra’ila za ta fara mahawara kan kwace yankin nan da mako mai zuwa.

Fiye da ‘yan majalisar Birtaniya 240 da ‘yan majalisar dattijan kasar sun rattaba hannu a wata wasika da ‘yan majalisun Tarayyar Turai fiye da dubu daya suka sanya wa hannu da ke Allah wadai da wani shirin Isra’ila na mamaye wasu yankuna na gabar yamma ta kogin Jordan.

Ministocin gwamnatin Isra’ila na iya fara mahawara kan aiwatar da wannan shirin nan da mako mai zuwa.

Wasikar ta fito karara ta na bayyana hadarin da ke tattare da daukan wannan matakin da Isra’ila ke son yi, wanda zai kwace kashi 30 cikin 100 na gabar yamma da kogin Jordan.

Wasikar ta nemi shugabannin kasashen Turai su dauki kwarararn matakai domin hana Isra’ila daukan wannan matakin, wanda suka ce zai kawar da sauran damar da ake da ita ta zaman lafiya tsakanin Falasdinawa da Yahudawa.

Cikin ‘yan majalisar Birtaniya da suke mara wa wannan wasikar baya akwai tsofaffin shugabannin jam’iyyun Conservative da na Labour kamar Lord Howard da Lord Kinnock, da kuma tsohon shugaban Kungiyar NATO Lord Robertson da ‘yan majalisa 35 na jam’iyyar Labour mai adawa.

Akwai kuma wasu tsofaffin ‘yan majalisar kasar Isra’ila da ke goyon bayan wannan yunkurin – kuma sun fito fili suna goyon bayan nemo wata hanya mafi adalci da za a bi wajen warware wannan matsalar.

Falasdinawa na kallon yankin a matsayin wanda za su shigar da shi cikin sabuwar kasar Falasdinu, kuma sun ki amincewa da yunkurin kwace shi da Isra’ila ke yi.

More News

EFCC ta kama wasu masu hada-hadar canjin kuÉ—aÉ—e

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta kama wasu mutane 34 da take zargi suna da hannu wajen yiwa...

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...