EFCC ta kama wasu masu hada-hadar canjin kuɗaɗe

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta’annati ta kama wasu mutane 34 da take zargi suna da hannu wajen yiwa darajar takardar kuɗin naira zagon ƙasa.

A wata sanarwa ranar Juma’a hukumar ta ce jami’anta dake sashin yaƙi da cin zarafin kuɗin naira, yawan amfani da dalar Amurka a mu’ammular kasuwanci a cikin gida Najeriya su ne suka samu nasarar kama mutanen.

Hukumar ta EFCC ta ce ta kama mutanen ne a yankin Wuse Zone 4 dake Abuja ranar 26 ga watan Afrilu.

EFCC ta ce nan bada jimawa za a gurfanar da mutanen a gaban kotu.

More News

Kotu ta bayar da belin Hadi Sirika da ƴarsa

Wata babbar kotun tarayya dake Abuja ta bayar da belin tsohon ministan harkokin sufurin jiragen sama, Hadi Sirika da kuma wasu mutane uku kan...

Kotu Ta Hana PDP Cire Shugaban Riƙon Jam’iyar

Wata Babbar Kotun Tarayya dake Abuja ta hana jam'iyar PDP dakatar da Umar Damagum daga matsayinsa na shugaban riƙon jam'iyar. Mai Shari'a  Peter Lifu shi...

Tinubu Ya Dawo Abuja Daga Ziyarar Aiki Da Ya Kai  Saudiya da Nezaland

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya dawo Abuja bayan ziyarar aiki da ya kai ƙasashen Saudiya da Nezaland. A ranar 22 ga watan Afrilu ne...

CBN ya dakatar da kudirinsa na sa bankuna su riƙa cajar kwastomominsu

Babban bankin Najeriya ya umarci bankunan da su dakatar da cajin kudaden ajiya har zuwa ranar 30 ga Satumba, 2024.Babban bankin ya bayyana hakan...