Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta’annati ta kama wasu mutane 34 da take zargi suna da hannu wajen yiwa darajar takardar kuɗin naira zagon ƙasa.
A wata sanarwa ranar Juma’a hukumar ta ce jami’anta dake sashin yaƙi da cin zarafin kuɗin naira, yawan amfani da dalar Amurka a mu’ammular kasuwanci a cikin gida Najeriya su ne suka samu nasarar kama mutanen.
Hukumar ta EFCC ta ce ta kama mutanen ne a yankin Wuse Zone 4 dake Abuja ranar 26 ga watan Afrilu.
EFCC ta ce nan bada jimawa za a gurfanar da mutanen a gaban kotu.