Kotu Ta Hana PDP Cire Shugaban Riƙon Jam’iyar

Wata Babbar Kotun Tarayya dake Abuja ta hana jam’iyar PDP dakatar da Umar Damagum daga matsayinsa na shugaban riƙon jam’iyar.

Mai Shari’a  Peter Lifu shi ne ya bayar da umarnin gaggawar a ranar 3 ga watan Mayu da ya hana jam’iyar zaɓar wani mutum domin ya maye gurbin Damagum har sai an kammala shari’ar da aka shiga gabansa.

Umar El-Gash Maina and Zanna Mustapha Gaddama sune suka shigar da ƙarar mai namba FCH/ABJ/CS/579/2024 a gaban kotun ranar 2 ga watan Mayu.

Waɗanda ake ƙara a shari’ar sun haɗa da kwamitin zartarwar jam’iyar, kwamitin amitattun jam’iyar, shugabannin jam’iyar da kuma hukumar zaɓe ta INEC.

Kotun ta dage sauraron ƙarar ya zuwa ranar 14 ga watan Mayu.

More News

Najeriya za ta dena shigo da man fetur a cikin watan Yuni – Dangote

Aliko Dangote mutumin da ya fi kowa arziki a Nahiyar Afirka ya ce Najeriya za ta daina shigo da man fetur a cikin watan...

An ceto mutane 9 daga wani ginin bene da ya ruguzo a jihar Niger

Mutane 9 aka samu nasarar cetowa daga wani ginin bene mai hawa ɗaya da ya ruguzo a yankin Sabon Gwari dake garin Minna babban...

An yi faɗa tsakanin masu sayar da waya da sojoji a kasuwar Abuja

Rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya, ta tura jami’an leken asiri zuwa kasuwar Banex – wata kasuwar kayan lantarki da na’urorin sadarwa da ke...

Yawan Mutanen Da Suka Mutu A Wutar Da Wani Matashi Ya Cinnawa Wani Masallaci A Kano Sun  Karu Zuwa 16

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon wutar da wani ya cinnawa wani masallaci a ƙauyen Gadan a...