INEC ta amince jam’iyu su cigaba da yakin neman zabe

Hukumar Zabe ta kasa INEC, ta ce a yanzu jam’iyun siyasa za su iya cigaba da yakin neman zabe gabanin sabuwar ranar da aka saka ta zaben shugaban kasa.

Hukumar ta bayar da wannan umarnin ne bayan wani taro da tayi ranar Litinin a Abuja.

Tun da farko shugaban hukumar, Mahmoud Yakubu ya ce ba za a cigaba da yakin neman zabe ba duk da dage ranar zaben shugaban kasa da na yan majalisun tarayya da aka yi.

Amma kuma bayan zaman ganawar da shugabannin hukumar suka yi hukumar ta ce yan takarar shugaban kasa da kuma jam’iyun siyasa za su cigaba da yakin neman zabe har ya zuwa daren ranar Alhamis.

Ko da a taron masu ruwa da tsaki na jam’iyar APC da ta gudanar a yau jam’iyar taci alwashin cigaba da yakin neman zabe duk da cewa hakan yaci karo da umarnin INEC.

Dokar zabe ta bayyana za a dakatar da yakin neman zabe ne sa’o’i 24 gabanin a fara kada kuri’a.

More News

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...