Human Rights Watch ta wallafa sabon rahoto |

Zargin da Isra’ilar ta musanta. Kungiyar ta Human Rights Watch ta bukaci kotun hukunta masu aikata manyan laifuffuka ta ICC, da ta bude sabon bincike kan lamarin. Mahukuntan na Palasdinawa sun yi marhabin da wannan rahoton, inda suka yi fatan duniya za ta yi wani hubbasa dagane da batun.

Daraktan kungiyar na yankin yahudawa da Palasdinawa Omar Shakir ya ce sun jima suna jan kunnen hukumomin Isra’ila kan abinda ke faruwa na nuna wariya, amma suka yi kunnen uwar shegu. Nuna wariyar launin fata da ya samo asali daga kasar Afirka ta Kudu, ba wai ya tsaya kan bakar fata ba kawai, lamari ne da a halin yanzu ka iya shafar kowa da kowa.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]