A yau ne yan takarar gwamnan jihar Kano a karkashin jam’iyu daban-daban suka rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya a karo na biyu.
Har ila yau suma shuwagabannin jam’iyu da suka tsayar da yan takara a zaben sun rattaba hannu kan jarjejeniyar wacce kwamtin zaman lafiya na zaben Kano ya shirya.
Kwamitin ya shirya bikin sanya hannun ne tare da hadin gwiwar kwamitin zaman lafiya na kasa da tsohon shugaban kasa, Abdulsalam Abubakar ke jagoranta.